An kaddamar da shirin samar da lantarki daga Najeriya zuwa wasu kasashe
Wallafawa ranar:
Kunna - 05:14
A ranar talata aka kaddamar da shirin samar da wutar lantarki daga Najeriya zuwa sauran kasashen yankin Yammacin Afirka, da suka hada da Nijar, Burkina Faso, Benin da kuma Togo da ake kira da suna 'West African Power Pool'.
Wannan dai shiri da za a kashe sama da dalar Amurka miliyan 568, wadanda za a samo daga Bankin Duniya, Kungiyar Turai, Hukumar Raya kasashe ta Faransa da kuma gwamnatin Najeriya.
Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Adamu Garba shugaban kamfanin IPI Group, kwararre kan harkar kimiya da wutar lantarki domin jin amfanin wannan shiri.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu