Naja'atu Muhammad: Kan afuwar da Buhari ya yi wa wasu 'yan siyasa
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:37
Kamar yadda watakila kuka ji a cikin labaran duniya, wasu Jami’an Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC da ICPC sun bayyana takaicinsu da matakin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dauka na yin afuwa ga wasu fitattun 'yan siyasar da aka yanke wa hukuncin dauri, inda suka zarge shi da zagon kasa akan aikinsu.
Wadannan jami’ai sun ce, matakin da shugaban ya dauka ya karya musu gwuiwa wajen gudanar da aikinsu, yayin da yan Najeriya ke ci gaba da bayyana korafi akan matakin afuwar.
Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hajiya Naja’atu Muhammad, Kwamishiniya a Hukumar kula da aikin Yan Sanda a Najeriya.
Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyar hirarsu
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu