Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Sojojin Ivory Coast 46 sun koma gida bayan shafe watanni 6 tsare a Mali

Wallafawa ranar:

Sojojin Ivory Coast 46 sun koma gida bayan shafe tsawon watanni 6 a hannun gwamnatin sojin Mali da ta tsare su kan zargin yi wa tsaron kasarta zagon-kasa, al’amarin da ya rura wutar gabar diflomasiya tsakanin kasashen biyu.

Shugaban Cote d'Ivoire Alassane Ouattara yayin maraba da sojojin kasar arba'in da shida da sojojin Mali suka yi wa afuwa, yayin da suka isa filin jirgin saman Felix Houphouet Boigny na kasa da kasa da ke Abidjan, Ivory Coast Janairu 7, 2023.
Shugaban Cote d'Ivoire Alassane Ouattara yayin maraba da sojojin kasar arba'in da shida da sojojin Mali suka yi wa afuwa, yayin da suka isa filin jirgin saman Felix Houphouet Boigny na kasa da kasa da ke Abidjan, Ivory Coast Janairu 7, 2023. © REUTERS/Luc Gnago
Talla

Da fari dai gwamnatin Mali ta yanke wa sojojin hukuncin daurin shekaru 20 a gidan yari, amma daga bisani ta yi musu afuwa bayan masu shiga tsakani sun sasanta su.

A game da wannan batu, Abdurrahman Gambo Ahmad ya tattuana da Al-Kasim Abdurrahman,mai sharhi kan al’amuran kasashen Afrika a Jamhuriyar Nijar

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.