Hukumar zabe a Najeriya ta bayyana Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben shugabancin kasar da akayi, yayin da wasu jam’iyyu ke korafi akan yadda hukumar taki sanya sakamakon zabe daga mazabu a rumbunanta kamar yadda tayi alkawari.
Wannan ne dalilin da ya as jam’iyyun PDP da Labour suka kauracewa cibiyar da aka ware ta musamman domin karbar da sakamakon zaben a Abuja.
Bayan gabatar da sakamakon, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Injiniya Yabagi Yusuf Sani, shugaban gamayyar jam’iyyun kuma ‘dan takaran zaben shugaban kasar a jam’iyyar APD.
Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu