Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Boulama Alhaji Gori kan halin da bakin haure ke ciki a iyakar Aljeriya

Wallafawa ranar:

Kungiyar agaji ta MSF, ta bukaci kasashe mambobin kungiyar ECOWAS ko CEDEAO, da su gaggauta kwaso dubban 'yan kasarsu, wadanda ke makale a lardin Assamaka da ke kan iyakar Aljeriya da Jamhuriyar Nijar.

'Yan sandan Morocco yayin kokarin hana daruruwan bakin-haure kwarara cikin yankin Melilla na kasar Spain.
'Yan sandan Morocco yayin kokarin hana daruruwan bakin-haure kwarara cikin yankin Melilla na kasar Spain. AP - Javier Bernardo
Talla

Bakin, wadanda yawan su ya kai kusan dubu biyar, sun samu kawunansu a cikin mawuyacin hali, bayan Aljeriya ta taso keyar su zuwa kasar Nijar.

Game da halin da bakin hauren ke ciki ne, Umar Sani ya tattauna da Boulama Alhaji Gori, mataimakin shugaban kula da ayyukan kungiyar MSF a yankin Afirka ta Yamma.

Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.