Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Dakta Ahmad Salisu kan gargadin gwamnatin Najeriya ga Peter Obi

Wallafawa ranar:

Gwamnatin Najeriya ta gargadi dan takarar shugabancin kasar a jam’iyyar Labour Party wanda ya sha kaye a zaben da ya gabata Peter Obi, da ya yi taka-tsantsa a game da kalaman da yake furta dangane da sakamakon wannan zabe,  wadanda a cewar gwamnati ka iya haddasa boren al’umma.  

Peter Obi kenan, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour ke kada kuri'arsa a Anambra. (2023/02/25)
Peter Obi kenan, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour ke kada kuri'arsa a Anambra. (2023/02/25) AP - Mosa'ab Elshamy
Talla

A lokacin wata ganawa da manema labarai a birnin Washington na kasar Amurka, ministan yada labaran Najeriya Alhaji Lai Muhammad, ya ce barazanar da Obi ya yi idan har aka rantsar da zababben shugaban kasar, kalamai ne da a gaban doka za a iya fassara su a matsayin cin amanar kasa.  

Kan haka ne Khamis Saleh ya tattauna da Dakta Ahmad Salisu Garba, masanin harkokin shari’a a kasar.  

Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.