Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Samaila Mohammed kan yadda matsalar bankuna ta shafi 'yan Najeriya

Wallafawa ranar:

Rahotanni daga Najeriya sun ce akalla kashi 40 na mutanen kasar da suka aike da sakwannin kudade ta waya daga cikin kashi 100 basu samu kudaden na su ba, kuma aiken bai kai ga mutanen da aka turawa ba. 

Yadda ake cirar kudi a na'urar bayar da kudi.
Yadda ake cirar kudi a na'urar bayar da kudi. © AFP/Pius Utomi Ekpei
Talla

Alkaluma sun nuna cewar yayin da aka samu karuwar aikewa da sakwannin kudaden ta wayoyin hannu, jama’a na shan wahala wajen samun kudadensu da suka makale a bankuna sakamakon irin wadannan sakwanni. 

Babban Bankin Najeriya a shekarar 2020 ya bai wa bankuna umurnin mayar wa jama’a kudadensu a cikin kasa da makwanni 2 idan an fuskanci irin wannan matsala. 

Dangane da wannan matsala, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziki,  Samaila Mohammed.

Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.