Tattaunawa da Hauwa Mustapha Babura kan sakin daliban kwalejin Yawuri a Kebbi
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:41
Rahotanni daga Najeriya sun ce anyi nasarar kubutar da sauran dalibai ‘yan mata guda 3 da suka rage a hannun ‘yan ta’addan da suka sace su a Kwalejin Yawuri ta jihar Kebbi cikin shekarar 2021.
Shugaban kungiyar iyayen daliban da aka sace, Salim Ka’oje ya sanar da sakin daliban guda 3 a ranar lahadin da ta gabata, bayan an biya kudin fansa.
Wadanda aka sake sun hada da Aliya Abubakar da Esther Sunday da kuma Elizabeth Nwafor.
Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da daya daga cikin mutanen da suka yi ta fafutukar ganin na kubutar da daliban Hauwa Mustapha Babura, mazauniyar kasar Amurka, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar......
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu