Ba don karfafa ni da Buhari ya yi ba, da na watsai da aikin gina matata mai..(Dangote)
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:46
Shugaban rukunonin kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya ce da ba don taimako da kuma kwarin gwuiwar da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi ta bashi ba, da ya dade da watsi da aikin gina matatarsa da aka kaddamar a Lagos saboda irin kalubalen da ya fuskanta.
Yayin da ya ke jawabi wajen bude matatar wanda ya samu halartar shugabannin kasashen Afirka da ‘yan kasuwa da kuma masu zuba jari, Dangote ya ce akwai lokacin da yayi tunanin dakatar da aikin baki daya. Dangane da tasirin matatar ga tattalin arzikin Najeriya da Afirka, Bashir Ibrahim Idris ya zanta da Dr Kasum Garba Kurfi, masanin tattalin arziki, kuma ga yadda zantawarsu ta gudana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu