Alhaji Muhammadu Magaji kan jan kafar da ake samu game da dokar ta baci kan abinci a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:40
Watanni 4 bayan kafa dokar ta baci da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi a bangaren samar da abinci, wasu jama’ar kasar na korafi cewar har yanzu basu ga tan 200 na hatsi da takin zamanin da ya ce a rabawa jama’a domin rage radadin talauci da karancin abincin da kasar ke fuskanta ba. Ya zuwa wannan lokaci farashin kayan abincin yayi tashin da ba’a taba gani ba, yayin da takin ya gagari talaka.
Dangane da wannan korafi, Bashir Ibrahim Idris ya tintibi Sakataren tsare tsare na kungiyar manoman Najeriya, Alhaji Muhammadu Magaji.
Ku danna alamar sauti don sauraron hirarar tasu......
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu