Ilimi Hasken Rayuwa
Kungiyar malaman jami'o'in Najeriya ta yi barazanar komawa yajin aiki
Wallafawa ranar:
Kunna - 10:00
Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' na wannan mako tare da Bashir Ibrahim Idris ya mayar da hankali ne kan barazanar da kungiyar malaman jami'o'in Najeriya ta yi na sake komawa yajin aiki. Malaman sun yi korafin cewa gwamnati ta ki cika alkawurran da ta dauka musu, sannan tana muzguna wa mambobinta.