Shirin ya duba yadda mata suka dukufa wajen neman aikin yi a Jamhuriyar Nijar
Wallafawa ranar:
Kunna - 09:58
Shirin na yau ya tabo batun yadda mata ke fafutukar dogaro da kai, yayin da suke fama da rashin aikin yi a Jamhuriyar Nijar.
Wannan na zuwa ne yayin da alkaluman marasa aikin yi, musamman mata ke kara yawaita, daidai lokacin da ake ci gaba da samun rashin aikin yi a kasashe masu tasowa musamman na Afirka.
Masana tattalin arziki sun jima suna jan hankalin gwamnatoci game da muhimmancin samar da guraben ayyukan yi ga matasa, musamman mata, duba da cewa suna bayar da gagarumar gudun mowa ga cigaban rayuwar al'umma.
Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin da Shamsiyya Haruna ta shirya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu