Shirin na wannan rana ya mayar da hankali ne kacokan kan tarin kalubalen da suke dabaibaye rayuwar mata a sassan daba-daban na duniya, musamman a kasashe matalauta.
‘Ya’ya mata a africa na fuskantar kalubane da dama a sha’anin rayuwar su ta yau da kullum, duk kuwa da cewar gwamnatocin kasashen na ta yunkurin dakile wadannan matsaloli
A shirin ci gaban cimma muradun karni da majalisar dinkin duniya ta samar waton SDgs, kudurori na daya da na biyu na magana ne akan yadda za'a kawar da talauci da yunwa a tsakanin al’umma.
Alkaluma da hukumar kididgar kasar Ghana ta GSS ta fitar sun nuna cewa, mata masu shekaru tsakanin 12 zuwa 17 sama da dubu 79 ne aka yiwa auren wuri ko kuma suke zaman daduro a kasar ta Ghana. Wadanda yawancinsu ke cewa talauci ne musabbabin daukar wannan mataki
Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin da Zainab Ibrahim ta gabatar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu