Isa ga babban shafi
EU-Jamus

Hannayen jarin Turai sun tashi bayan Jamus ta amince sake ceto Tattalin arzikin Turai

Kasuwannin hannayen jarin turai sun tashi sama bayan da Majalisar dokokin kasar Jamus ta amince da shirin fadada karfin Kungiyar Tarayyar Turai kan asusun tallafawa matsalar tattalin arziki.Kada kuri’ar ta zama gwaji ga Shugaban gwamnatin kasar Angela Merkel, yayin da wasu da ke cikin gwamnatin hadakar suka yi adawa da tsarin.Yan majalisa 523 suka amince da tsarin, 85 suka kada kuri’ar adawa, uku basu jefa kuria ba, yayin da tara suka kauracewa zaman majalisar mai wakilai 620.A kasar Girka mai fama da matsalar tattalin arziki, an gudanar da zanga zanga, sakamakon ziyarar masu bincike na kasashen duniya kan yiwuwar sake bai wa kasar kudaden tallafi. 

Ginin Babban Bankin kasashen Turai
Ginin Babban Bankin kasashen Turai Reuters/Ralph Orlowski
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.