Isa ga babban shafi
Faransa

Kotu ta mika dukiyar Lilian ga ‘Yar ta

Wata Kotu a Faransa ta sanya kula da dukiyar hamshakiyar Attajirar kasar, Lilian Bettencourt, a hannun ‘Yar ta, da jikokinta , saboda abinda suka kira tabarbarewar lafiya da kuma dimbin shekaru.Kotun tace, daga yanzu, Francoise, da kuma jikokin ta zasu dinga tafiyar da dukiyar da ta kai Euro biliyan 16, abinda lauyanta yace bai amince ba, kuma zai daukaka kara.Ita Lilian Bettencourt ta na da shekaru 88, kuma sun dade suna takaddama da yar, kan yadda ta ke yin kyauta dukiyarta ta fitar hankali, abinda Yar ke cewa, wani shiri ne na rabe dukiyar. 

Lillian Bettencourt
Lillian Bettencourt REUTERS/Charles Platiau/Files
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.