Isa ga babban shafi
Libya-Rasha-Belarus-Ukraine

Kotun Libya ta yanke wa wasu Turawa hukuncin dauri a gidan yari

Wata kotun Soji a kasar Libya ta yankewa wasu Turawan Ukraine 19 da wasu uku ‘yan kasar Belerus da Biyu ‘Yan Rasha hukuncin dauri a gidan yari bayan kama su da laifin zama Sojojin haya na Kanal Gaddafi a rikicin kasar.

Alkalin Alakalai kotun kolin Libya, Kamal Bashir Dahan a lokacin da yake ganawa da Mambobin kwamitin kundin tsarin mulkin kasar
Alkalin Alakalai kotun kolin Libya, Kamal Bashir Dahan a lokacin da yake ganawa da Mambobin kwamitin kundin tsarin mulkin kasar REUTERS/Ismail Zitouny
Talla

Daga cikinsu Turawan, an yankewa wani Dan Rasha hukuncin daurin Rai-da Rai a gidan yari sauran kuma aka yanke masu hukuncin daurin shekaru 10.

Sai dai dukkanin Turawan sun musanta zargin da kotun ke masu inda suka ce su ma’aikata  da ke aiki a bangaren man fetir.

A zaman kotun, Akwai jakadun kasashen Ukraine da Belarus wadanda suka ce zasu daukaka kara.

Wani kakakin gwamnatin Libya yace tun Ogustan bara ne  aka cafke Turawan a birnin Tripoli.

Akwai dai hulda tsakanin gwamnatin Ukraine da Gaddafi, kuma an kiyasta akwai kimanin ‘Yan kasar Ukriane 1,500 da ke zama a Libya kafin barkewa rikici a tsakiyar Febrairun shekarar 2011.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.