Isa ga babban shafi
Ukraine-Amurka-Rasha

Joe Biden ya isa Kiev domin ziyarar aiki

Mataimakin shugaban Amurka Joe Biden ya isa birnin Kiev na kasr Ukraine domin gudanar da ziyarar aiki, ziyarar da ke zuwa ne a daidai lokacin da masu ra’ayin Rasha ke ci gaba da tayar da kayar baya da kuma mamaye manyan cibiyoyin gwamnati a wasu biranen gabashin Ukraine.

Joe Biden mataimakin shugaban kasar Amurka
Joe Biden mataimakin shugaban kasar Amurka REUTERS/Kacper Pempel (
Talla

A wata sanarwa da ta fiyar kuwa, gwamnatin Rasha ta zargi hukumomin birnin Kiev da karya yarjejeniyar da aka cimma a birnin Geneva cikin makon da ya gabata, wadda ta shata yadda za a warware sabanin da ke tsakanin Ukraine da kuma Rasha.

Ko shakka babu dai ana kallon wannan ziyara ta mataimakin shugaban Amurka Mista Biden a matsayin kara jaddada goyon Amurka ga Ukraine.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.