Birni Paris na fatar shirya gasar Olympics na shekara ta 2024
A Faransa fadar Magajin garin Paris bisa Shugabanci uwargida Anne Hidalgo ta bayana fatar gani hukumar Olympic ta baiwa birni Paris damar karbar bakuncin wasannin Olympic na shekara ta 2024.Sanarwa dake zuwa a dai de lokacin da fadar Shugaban kasar ta sanar da bada na ta goyan baya a kai.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Mahimanci haka ya sa magajiyar birni Paris Anne Hidalgo bayana fari cikin tareda yabawa matakin da wakilan birni Paris suka cima dama neman goyan bayan daukacin mutanen kasar.
A dai wajen fadar Shugaban kasar ta sanar da ziyarar da shugaba Francois Hollande zai kaiwa birni Lausanne na kasar Swiziland domin kawo nasa kwarin guiwa dama tattaunawa da hukumomin Olympics.
Biranen Boston na kasar Amaruka, Hambourg daga Jamus da birni Roma na Italiya na cikin sahu kasashe dake fatar gani sun karbi bakuncin wasannin Olympic na shekara ta 2024.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu