Isa ga babban shafi
Turkiya

Ana zaben Majalisar Dokoki a kasar Turkiyya

A wannan lahadi sama da mutane milyan 53 ne ke jefa kuri’unsu a zaben ‘yan majalisar dokokin kasar Turkiyya, zaben da ake kallo a matsayin zakaran gwajin dafi ga shugaba Racep Tayyip Erdogon, kasantuwarsa zaben majalisa na farko da ake gudanarwa tun bayan da ya karbi ragamar shugabancin kasar.

Magoya bayan shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan
Magoya bayan shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan REUTERS/Murad Sezer
Talla

Jam’iyyar Erdogon dai na bukatar kujeru 330 daga cikin 550 domin ci giaba da kasancewa mai rinjaye a cikin zauren majalisar.

To sai dai manazarta al’amurran siyasar kasar ta Turkiyya na ganin cewa ko a wannan karo jam’iyyar AKP ta shugaban za ta iya yin nasara a zaben.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.