Isa ga babban shafi
Spain

Mutane 35 sun hallaka a teku tsakanin Spain da Maroko

Jami’an tsaron gabar ruwan kasar Spain sun dakatar da aikin ceto domin gano wasu mutane 35 da suka bata sakamakon nutsewar kwale-kwalen da suke tafiya a cikinsa tsakanin kasar ta Spain da kuma Maroko.

Afghanawa bakin haure a kan teku
Afghanawa bakin haure a kan teku (©Reuters)
Talla

Mai magana da yawun hukumar tsaron gabar ruwan kasar da farko ta sanar da cewa an ceto mutane 15 da rayukansu, yayin da har yanzu ba a gano wasu 35 ba.

Rahotanni sun ce ‘yan ci-ranin da lamarin ya shafa sun fito ne daga kasashen Cote d’Ivoire, Nigeria, Mali, Guinea da kuma Kamaru.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.