Isa ga babban shafi
Faransa

Dubban Jama'a suka shiga Zanga-Zangan Faransa

Mutane akalla 100  ‘Yan sandan Faransa suka kama yayin zanga-zangan a birnin Paris inda dubban mutane suka shiga zanga-zangan don adawa da sabon dokan kodago dake shan suka a kasar

Masu zanga-zanga a birnin Paris
Masu zanga-zanga a birnin Paris AFP/KENZO TRIBOUILLARD
Talla

‘Yan sandan kwantar da tarzoma akalla 2,000 suka ja daga a sassan birnin Paris domin kare zanga-zangan lumana daga kazancewa,a lokacin da aka fara kwana hudu da fara gasan wasannin kwallon kafan cin kofin Turai da ake bugawa yanzu haka.

Zanga-zangan dai bai kazance ba sosai kasancewar masu zanga-zangan kan rika mikawa ‘yan sanda furanni ne mayayin da suke maci.

Ministan harkokin cikin gida Bernard Caseneuve ya bayyana cewa anyi zanga-zangan cikin natsuwa tunda dai ‘Yan sanda basu yi amfani da barkonun tsohuwa ba, kuma babu wanda ya jikkata.

Hukumomin Faransa na cewa mutane akalla dubu 70 suka shiga zanga-zangan a fadin kasar Alhamis din nan, kodashike kungiyar Kodago na cewa mutane dubu 200 suka shiga.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.