Isa ga babban shafi
Vatican

Paparoma Francis ya nemi a yi zaman lafiya a Congo

Shugaban darikar Katolika a Duniya Paparoma Francis a yau lahadi ya yi kira na a rungumi zaman lafiya a yankin Kasai na Jamhurriyar Demokradiyar Kongo dake fama da tashe tashen hankula.

Paparoma Francis ya nemi a yi zaman lafiya a Congo
Paparoma Francis ya nemi a yi zaman lafiya a Congo REUTERS/Alessandro Bianchi/File Photo
Talla

Paparoman ya yi wannan kiran ne a yayin da yake jawabi ga mabiya addinin Krista a Capri dake arewacin kasar Italiya inda aka fuskanci munmunar girgizar kasa har sau biyu a shekarar 2012.

Paparoma Francis ya shawarci al’ummar duniya da su mayar da hankali wajen rokon Allah don samun zaman lafiya da kuma sauya tunanin wadanda ke tada zaune tsaye.

Mutane akalla dari hudu ne suka mutu a rikice rikice da aka kwashi sama da watanni shida ana yi a yankunan yammancin Kasai da Lomami dake Jamhurriyar Demokradiyar Kongo cikinsu har da kwararrun ma’aikatan Majalisar Dinkin Duniya guda biyu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.