Isa ga babban shafi
Belgium

Wani matashi ya kai wa sojin Belgium farmaki

Jami’an sojin kasar Belgium sun bude wuta kan wani mutum a tsakiyar birnin Brussels, a daren jiya Juma’a, bayanda ya afka musu da sara, a guje, rike da wuka, yana Kabbara.

Jami'an soji dana 'yan sandan kasar Belgium a wurin da matashi dan kasar Somalia ya kai wa jami'an tsaron hari da wuka a birnin Brussels, ranar 25 ga watan Agustan shekarar 2017.
Jami'an soji dana 'yan sandan kasar Belgium a wurin da matashi dan kasar Somalia ya kai wa jami'an tsaron hari da wuka a birnin Brussels, ranar 25 ga watan Agustan shekarar 2017. Thomas Da Silva Rosa /REUTERS
Talla

Jami’an soji biyu ne suka samu raunuka sakamakon harin, inda daya ya samu rauni a hannu, dayan kuwa a fuska, sai dai raunukan basu yi muni ba.

Matashin mai shekaru 30, wanda dan asalin kasar Somalia ne, ya mutu, jim kadan bayan da aka garzaya da shi asibiti.

A rahoton da suka fitar hukumomin tsaron kasar ta Belgium, sun ce matashin bashi da tarihin wata alaka da kungiyoyin ‘yan ta’adda ko kuma yinkurin hakan, sai dai sun dauki harin a matsayin na ta’addanci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.