Faransa ta girmama Arnaud Beltrame
Hukumomin Faransa a yau laraba sun girmama dan sandan kasar Arnaud Beltrame mutum na hudu da ya rasa ransa sakamakon harin da wani dan bindiga ya kai kan wani katafaren kanti a kudancin Faransa.
Wallafawa ranar:
Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya yaba da jan kokarin Beltrame, Macron ya bayyana shi a matsayin jarumi.
Idan aka yi tuni dan bindigar ya harbe shi tare da caka masa wuka, Beltrame ya mika kansa ne cikin kantin, domin fansar wata Mata da maharin ya yi garkuwa da ita, kafin daga bisani jami’an tsaro su hallaka dan bindigar.
Shugaban kasar Emmanuel Macron ya ce Beltrame ya sadaukar da ransa ga kasarsa Faransa, kuma baza’a manta da bajintarsa ba.
Dubban Faransawa ne suka halara a wannan wuri na place des Invalides domin girmama kanal Arnaud Beltrame.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu