Isa ga babban shafi
Nagorno-Karabakh

Rasha ta zargi Azarbaijan da karya yarjejeniyar tsagaita wuta a Karabakh

Rasha ta zargi Azabaijan da karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta hanyar shiga yankin da a yanzu ke karkashin kulawar dakarunta na wanzar da zaman lafiya a yankin Nagorno-Karabakh, inda Azerbaijan din ta gwabza yaki da Armenia kan mallakarsa.

Wasu ginegine da hare-haren soji suka ragargaza a garin Ganja, da ke yankin Nagorno-Karabakh a kasar Azerbaijan. A ranar 11, ga Oktoban shekarar 2020.
Wasu ginegine da hare-haren soji suka ragargaza a garin Ganja, da ke yankin Nagorno-Karabakh a kasar Azerbaijan. A ranar 11, ga Oktoban shekarar 2020. © REUTERS/Umit Bektas
Talla

Karon na farko kenan da Rasha ta fito fili ta dora laifin karya yarjejeniyar tsagaita wutar ta 2020 kan Azerbaijan.

Ma'aikatar tsaron Rasha ta kuma zargi sojojin kasar ta Azarbaijan da yin amfani da jirage marasa matuka da Turkiyya ta kera wajen kai farmaki kan dakarun Armenia a Karabakh.

Sai dai ma'aikatar tsaron Azerbaijan ta musanta zargin da Rasha ke mata, inda tace Armenia ce ke yunkurin tada hankali ta hanyar kin janye sojojinta daga yankin na  Karabakh.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.