Isa ga babban shafi

Sama da mutane dubu 250 sun yi zanga-zangar adawa da masu ra'ayin mazan jiya a Jamus

Kimanin mutane dubu dari 2 da 50 ne suka fito zanga-zanga a fadin Jamus a jiya Asabar don nuna rashin amincewa take-taken jaam’iyya mai ra’ayin mazan jiya  na AFD, wadda ta janyo cece-kuce bayan da aka samu bayanan da ke nuni da cewa mambobinta sun tattauna shirin tisa keyar  baki a wani taro na masu tsatsauran ra’ayi.

Wasu masu zanga-=zanga a birnin Berlin na Jamus.
Wasu masu zanga-=zanga a birnin Berlin na Jamus. AP - Christoph Soeder
Talla

Dubban mutane ne suka fito a biranen Frankfurt, Hanover da Dortmund, suna daga kwalayen da ke dauke da rubutun nuna adawa da jam’iyyar ADF.

 

Tun daga ranar Juma’a aka yi kiran zanga-zanga a wurare dabam -dabam har dari a fadin kasar Jamus, ciki har da birnin Berlin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.