Isa ga babban shafi
Equatorial Guinea

Equatorial Guinea ta raba gari da kocinta

Kocin kasar Equatorial Guinea Henri Michel, dan kasar Faransa ya ajiye aikin shi, wata daya a fara gudanar da gasar cin kofin Afrika inda kasar ke daya daga cikin masu daukar nauyin gudanar da gasar.

Dan kasar Faransa Henri MIchel Kocin Equatorail Guinea.
Dan kasar Faransa Henri MIchel Kocin Equatorail Guinea. AFP/PHOTO/ABDELHAK SENNA
Talla

Mista Michel wanda tsohon jagoran ‘yan wasan Faransa ne kuma tsohon koci ya ajiye aikinsa ne bayan da wani babban jami’in hukumar wasanin kasar ya nemi ya yi masa katsalandan ga aikinsa na shirye shiryen gudanar da gasar Cin kofin Nahiyar Afrika da za’a fara a ranar 21 ga watan Janairu.

Yanzu haka kuma hukumar wasannin ta maye gurbin Michel da Casto Nopo a matsayin sabon koci.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.