An dage takunkumi kan Meng ‘Yar tseren daben santsi a kasar Sin
Shahararren ‘Yar wasan tseren daben santsin kasar Sin din nan, Wang Meng, za ta dawo karawa a fagen wasan tsere bayan an dage wani takunkumi da ya hanata yin gasa ma kasarta na tsawon watanni 13.
Wallafawa ranar:
Ita dai Meng, ‘Yar shekaru 27, wacce kuma keda lambobin yabo da ta samu a wasannin Olympic guda hudu, ta yi fada ne da manajanta don ya mata fada akan ta dawo masaukin ‘Yan wasan kasar ta Sin a latti.
Wannan dai bashi ne karo na farko da Meng ke fada da manyan hukumar wasannin kasar ba, domin a shekarar 2007 an taba korarta daga cikin ‘Yan wasan kasar Sin na tsawon watanni shida bayan ta yi suka da yadda kocinta ke horar dasu.
Dawowar Meng, karawa a fagen tsere na nufin za ta wakilici kasarta a gasar wasannin da za a yi a kasar Rasha a shekarar 2014.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu