Isa ga babban shafi
Kwallon kafa

Liverpool ta amince Luis Suarez ya tattauna da Arsenal

Kungiyar Liverpool ta kasar Ingila ta ce ta amince dan wasanta Luis Suarez ya bude tattaunawa da kungiyar Arsenal wacce ta taya shi akan kudi miliyan 40 na kudin pam din Ingila.  

Dan wasan Liverpool Luiz Suarez
Dan wasan Liverpool Luiz Suarez REUTERS/Nigel Roddis
Talla

Wannan tayi na Arsenal ya bude wata dama ce da za ta bawa dan wasan ficewa daga kungiyar ta Liverpool amma hukumomin kungiyar sun ce kudin da Arsenal din ta yi tayin ya yi kadan.

Rahotanni na nuna cewa, Liverpool na neman kudi miliyan 50 ne na pam din Ingila.

A daya bangaren a jiya ne Suarez ya dawo bugawa Liverpool wasa bayan kammala hukuncin da ya haramta mai buga wasannin guda goma da aka zartar bayan an same shi da laifin cizon dan wasan Chelsea, Branislav Ivanovic a kakar wasan da ta gabata.

Liverpool ta buga wasan sada zumunci ne da Melbourne Victory inda ta lallasa ta da ci 2-0.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.