Kwallon kafa
Ghana da Algeria za su je Brazil 2014
Kasashen Ghana da Algeria sun mallake sauran gurabe biyu da suka rage a wasannin neman shiga gasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Algeria dai ta lallasa Burkina Faso ne da ci 1-0 yayin da Ghana duk da cewa ta sha kashi a hanun Masar da ci 2-1 itama ta samu tsallakawa zuwa gasar idan aka yi jumallar kwallaye da ta zira wasan farko.
Tun a karshen makon da ya gabata ne Najeriya, Cote’d Ivoir da Kamaru suka samu gurabensu.
Wannan gasa ta cin kofin duniya za ta kasance muhimmiya musamman ga kasar Ghana ganin cewa a wannan karo ne za ta fara zuwa da mai horar da ‘yan wasa na gida.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu