Isa ga babban shafi
Champions League

An hada City da Barcelona, Arsenal da Bayern Munich

Kungiyar Barcelona za ta kara da Manchester City a zagaye na biyu a gasar zakarun Turai, yayin da mai rike da kofin gasar Bayern Munich aka sake hada ta wasa da Arsenal karo na biyu a jere. Ana ganin wadannan ne wasanni mafi zafi da za'a gudanar a zagaye na biyu.

Mai horar da 'yan wasan Bayern Munich, Pep Guardiola Tsohon kocin Barcelona yana mika wa kocin Arsenal Arsene Wenger hannu a lokacin wasa tsakanin Barcelona da Arsenal
Mai horar da 'yan wasan Bayern Munich, Pep Guardiola Tsohon kocin Barcelona yana mika wa kocin Arsenal Arsene Wenger hannu a lokacin wasa tsakanin Barcelona da Arsenal skysport
Talla

Kungiyoyin Ingila Manchester United da Chelsea, sun samu sassauci daga kungiyoyin da aka hada su wasa a zagaye na biyu inda aka hada Manchester United wasa da Olympiakos ta Girka Chelsea kuma da Galatasaray ta Turkiya.

Kungiyar Paris Saint-Germain ta Faransa an hada ta wasa ne da Bayer Leverkusen ta Jamus, AC Milan kuma za ta kara ne Atletico Madrid.

An hada Real Madrid ne da Schalke 04 yayin da Borussia Dortmund zata kara da Zenit St Petersburg.

Didiar Drogba zai kai ziyara a Stamford Bridge inda Chelsea zata fara karbar bakuncin Galatasaray. Yaya Toure kuma zai kara ne da Tsohuwar kungiyar shi Barcelona.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.