Isa ga babban shafi
FIFA

Costa zai fara taka kwallo a Spain

Diego Costa dan asalin kasar Brazil malamin raga a kungiyar Atletico Madrid zai fara bugawa Spain kwallo a karawar sada zumunci da Italiya bayan ya yi watsi da kasarsa Brazil.

Diego Costa Dan wasan Atlético Madrid.
Diego Costa Dan wasan Atlético Madrid. REUTERS/Susana Vera
Talla

Spain zata kara ne da Italiya a ranar Laraba kungiyoyin da suka buga wasan karshe a gasar cin kofin Turai. Ana sa ran bayan kammala wasan kasashen zasu fitar da ‘Yan wasan da zasu kai ziyara a kasar Brazil a gasar cin kofin duniya.

A yau Talata, ya rage kwanaki 100 cur a fara gasar cin kofin Duniya a kasar Brazil. Kuma Samba boys ne na Brazil zasu fara karawa da Croatia a ranar 12 watan Yuni.

Costa ya taba sanya rigar Brazil a wasannin sada zumunci amma daga bisani dan wasan ya amince ya buga wa Spain kwallo.

A tsarin Hukumar FIFA, sai idan Dan wasa ya sanya riga a wata gasa shi ne ba zai iya canza sheka ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.