Isa ga babban shafi
CAF

TP Mazembe ta lashe kofin zakarun Afrika

Kungiyar TP Mazembe ta lashe kofin gasar zakarun Afrika bayan ta doke USM Alger ta Algeria da jimillar kwallaye 4 da 1. A jiya Lahadi Mazembe ta doke Alger ne 2 da 0 a fafatawar da suka yi a Jamhuriyyar Congo bayan ta samu nasara a karshen makon da ya gabata ci 2 da 1 a Algeria.

Karo Biyar TP Mazembe na lashe kofin zakarun Afrika
Karo Biyar TP Mazembe na lashe kofin zakarun Afrika AFP PHOTO / JUNIOR KANNAH
Talla

Wannan ne karo na biyar da TP Mazembe ke lashe kofin gasar zakarun Afrika. Yanzu kungiyar ta yi kafada da Zamlek ta Masar, wadanda ke bayan Al Ahly da ta lashe kofin sau 8.

Kungiyar TP Mazembe ita za ta wakilci Afrika a gasar cin kofin zakarun kungiyoyin kwallon kafa a duniya da za buga a Japan, inda kungiyar za ta gamu da irinsu Barcelona.

A 2010 Mazembe ta buga wasan karshe da Inter Milan a gasar zakarun kungiyoyin kwallon kafa na duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.