Isa ga babban shafi
Wasanni

Gasar Turai: Arsenal da Chelsea sun kai matakin gaba

Kungiyoyin kwallon kafa na Arsenal da Chelsea sun tsallaka zuwa matakin gaba na kungiyoyi 16 da za su ci gaba da fafatawa a gasar cin kofin zakarun Turai bayan sun samu nasara a wasanninsu na jiya.

'Yan wasan Arsenal Olivier Giroud da Per Mertesacker bayan sun samu nasara akan Olympiakos a jiya
'Yan wasan Arsenal Olivier Giroud da Per Mertesacker bayan sun samu nasara akan Olympiakos a jiya Reuters / Andrew Couldridge
Talla

Arsenal ta doke Olympiakos da ci 3-0 yayin da Chelsea ta casa FC Porto da ci 2-0.

Tuni dai kocin Chelsea Jose Mourinho ya yi fatan cewa, nasarar da kungiyarsa ta samu za ta maido wa ‘yan wasansa da kuzarinsu da suka rasa a baya, wanda hakan ne ya ke ganin zai taimaka masa har ya ci gaba da zama a matsayin Coci a kungiyar.

Chelsea dai ta gamu da koma baya matuka a wannan kakar, abin da ya sa ake ganin za a iya koran sa daga kungiyar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.