Al Ahly ta Masar ta dauki Martin Jol a matsayin kocinta
Kungiyar kwallon kafa ta Al Ahly da ke Masar ta sanar da daukan Martin Jol a matsayin sabon mai horar da ‘yan wasanta, inda ya maye gurbin Abdel Aziz Abdel Shafy wanda ya jagorance ta a matsayin kocin rikon kwarya.
Wallafawa ranar:
Sanarwar dai na zuwa ne bayan Jol mai shekaru 60 ya amince da kulla kwantiragi da kungiyar, kuma tuni ya gana da shugabanta Mahmoud Taher a birnin London a cikin wannan makon.
Martin Jol dai ya horar da Fulham gabanin ya raba gari da ita a watan Disamban shekarar 2013 bayan ta sha kashi a wasanni shida a jere a gasar Premier ta Ingila.
Sannan ya horar da Tottenham da Ajax da kuma Hamburg ta Jamus.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu