Isa ga babban shafi
Wasanni

FIFA ta amince da kasashe 48 a gasar kofin duniya

Hukumar kwallon kafa ta duniya ta amince da matakin fadada gasar cin kofin duniya da ake gudanarwa duk bayan shekaru hur-hudu, in da daga shekarar 2026, kasashen duniya 48 za su rika fafatawa a babbar gasar.

Shugaban FIFA Gianni Infantino ne ya gabatar da kudirin fadada gasar cin kofin duniya
Shugaban FIFA Gianni Infantino ne ya gabatar da kudirin fadada gasar cin kofin duniya REUTERS/Arnd Wiegmann
Talla

A yau Talata ne mambobin hukumar ta FIFA suka kada kuri’ar amincewa da kudirin wanda shugaban hukumar Gianni Infantino ya gabatar.

Yanzu haka dai za a rika gudanar da jumullar wasanni 80 a gasar a maimakon 64 da aka saba yi, in da kasashe 32 ke fafatawa da juna.

Kazalika za a rika kammala gasar ta cin kofin duniya a cikin kwanaki 32 da zaran an fara aiwatar da matakin.

A karo na farko kenan tun shekarar 1998 da aka fadada gasar cin kofin duniya, abin da zai bai wa kasashen da ba su taba halarta ba a can baya, damar shiga domin a dama da su.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.