CAF
Gabon 2017: Masar ta doke Ghana, an fitar da Mali da Uganda
Masar ta doke Ghana ci 1 da 0 a kawarar da suka yi jiya a gasar cin kofin Afrika da ake gudanarwa a Gabon. Amma dukkaninsu sun tsallake zuwa zagayen kwata fainal.
Wallafawa ranar:
Talla
An yi fitar da Mali da Uganda wadanda suka tashi kunnen doki a karawar da suka yi a jiya.
Masar ce ta jagoranci teburin rukuninsu na D da maki 7, Ghana kuma ta tsallake ne da maki 6.
Yanzu Masar za ta hadu ne da morocco a ranar lahadi a wasan kusa da karshe. Ghana za ta hadu ne da Jamhuriyar Dimokuradiyar Congo.
A ranar Asabar ne Burkina Faso za ta kara da Tunisia. Senegal kuma da Kamaru.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu