Najeriya da Kamaru sun kai zagayen gaba a gasar kofin duniya
Kasashen Najeriya da Kamaru sun samu gurabe a zagaye na biyu na gasar cin kofin duniya ta mata da ke gudana a Faransa kuma a karon farko kenan a tarihin gasar da kasashen Afrika guda biyu ke tsallakawa zuwa wannan mataki na kasashe 16 da za su ci gaba da karawa da juna.
Wallafawa ranar:
Kasar Kamaru ta samu gurbinta ne bayan ta samu nasarar doke New Zealand da kwallaye 2-1 a ranar Alhamis, kwallayen da Ajara Nchout ta ci wa Kamarun.
Ita kuwa Super Falcons ta Najeriya ta kai matakin ne bayan kasar Chile ta gaza doke Thailand da kwallaye 3-0, inda ta samu nasara akan Thailand din da ci 2-0, abinda ya sa Najeriyar ta samu gurbin.
Yanzu haka Najeriya za ta hadu da Jamus a gobe Asabar, yayinda Kamaru za ta hadu da Ingila a ranar Lahadi.
A karon farko kenan cikin shekaru 20 da Najeriya ke kai wa matakin zagaye na biyu na gasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu