Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon kafa

Za a sake yi wa Osimhen gwajin Korona

Kungiyar kwallon kafa ta Napoli ta tabbatar da cewa za a sake yi wa dan wasanta, Victor Osimhen gwajin cutar coronavirus, saboda har yanzu cutar ba ta rabu da shi ba.

Victor Osimhen dan wasan Najeriya da ya sauya sheka daga kungiyar Lille dake Faransa, zuwa Napoli a Italiya.
Victor Osimhen dan wasan Najeriya da ya sauya sheka daga kungiyar Lille dake Faransa, zuwa Napoli a Italiya. AFP/JEAN-FRANCOIS MONIER
Talla

Gwanji ya tabbatar dan shekarau 22 din ya harbu da cutar covid 19 ne jim kadan bayan dawowarsa daga kasarsa, Najeriya, inda ya je hutun Kiristimeti.

An yi zargin cewa dan wasan ya kamu da wannan cuta ne sakamakon yin watsi da ka’idojin da aka gindaya don dakile ta, a yayin da ya yi bikin tunawa da ranar haihuwarsa a 29 ga watan Disamba, lamarin da ya nemi afuwa a kai.

Dan wasan tawagar kwallon kafar Najeriyar ya kebe kansa na tsawon kwanaki 14, amma bayan an sake gwada shi sai aka ga burbushin cutar a tattare da shi.

A shafinta na Twitter, kungiyar Napoli ta nanata cewa za a sake yi wa dan wasan gwajin Covid 19.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.