Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon Kafa

Messi da Ronaldo sun samu koma baya a jerin wadanda za su lashe Balon d'Or

Shahararrun ‘yan wasan kwallon kafa, Lionel Messi da Cristiano Ronaldo da Neymar sun samu koma baya a jerin ‘yan wasan da ake sa ran za su lashe kyautar gwarzon dan kwallon duniya ta Balon d’Or ta shekarar 2021.

Lionel Messi da Cristiano Ronaldo yayin wani wasan El Clasico match
Lionel Messi da Cristiano Ronaldo yayin wani wasan El Clasico match Reuters
Talla

Messi wanda shi ke rike da kambun, kuma sau 6 yana lashe kyautar  yana matsayi na 3 a cikin jerin ‘yan wasa 20 da aka fitar, yayin da Cristiano Ronaldo, wanda sau 5 ya ci kyautar yana matsayi na 8 sai Karim Bnezema a matsayi na 9.

Neymar Junior yana matsayi na 19, Luka Modric na matsayi na 15, Luiz Suarez na lamba 13.

Robert Lewandowky, dan wasan Bayern Munich yana matsayi na 1, sai Kylian Mbappe na PSG da Faransa na a matsayi na 2.

A watan Disamba ne za bayyana wanda ya lashe kyautar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.