Isa ga babban shafi
Wasanni - Gasar Cin Kofin Turai

UEFA ta baiwa birnin Rome damar karbar bakuncin gasar Euro 2020

Hukumar kwallon kafa ta Turai UEFA ta tabbatar da birnin Rome a matsayin wanda zai karbi bakuncin gasar cin kofin kasashen Turai ta Euro 2020, wadda aka sauya lokacinta na gudana daga shekarar ta bara zuwa bana saboda annobar Korona.

Virginia Raggi, magajiyar garin birnin Rome a kasar Italiya, yayin gabatar da jawabi kan shirin karbar bakuncin wasannin gasar cin kofin kasashen Turai ta Euro 2020.
Virginia Raggi, magajiyar garin birnin Rome a kasar Italiya, yayin gabatar da jawabi kan shirin karbar bakuncin wasannin gasar cin kofin kasashen Turai ta Euro 2020. AP - Andrew Medichini
Talla

Jadawalin gasar cin kofin kasashen Turan dai ya nuna cewar, birnin na Rome ne zai karbi bakuncin wasannin farko da za su gudana a gasar da hadin gwiwar kasashen Turkiya da Italiya za su karbi bakunci.

A nasu bangaren kuma hukumomin kasar Italiya sun bada tabbacin cewar za a baiwa ‘yan kallo damar baiwa idanunsu abinci kai tsaye yayin wasannin da za su gudana a babban filin wasan birnin na Rome.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.