Isa ga babban shafi

Koeman zai ci gaba da jagorancin Barcelona - Laporta

Shugaban kungiyar kwallon kafar Barcelona dake kasar Spain Joan Laporta ya bayyana cewar Ronald Koeman zai cigaba da jagorancin kungiyar a kaka mai zuwa duk da korafe korafen da wasu Yan wasa da magoya bayan kungiyar ke yi.

Ronald Koeman ya samu goyan bayan shugabannin Barcelona -Joan Laporta
Ronald Koeman ya samu goyan bayan shugabannin Barcelona -Joan Laporta JOSE JORDAN AFP/File
Talla

Bayan wani taron Daraktocin kungiyar da aka gudanar yau, Laporta yace sun yanke hukuncin baiwa Koeman karin damar cigaba da jagorancin kungiyar kamar yadda kwangilar shi ta nuna.

Shugaban kungiyar yace suna da yakinin cewar matakin da suka dauka na cigaba da tafiya da Manajan shine mafi alheri a gare su da Barcelona kuma suna farin ciki da haka.

Dan wasan Celta Denis Suárez yana kokarin tare Lionel Messi na Barcelona
Dan wasan Celta Denis Suárez yana kokarin tare Lionel Messi na Barcelona Pau BARRENA AFP

Laporta yace babu tantama sun tattauna matsayin Koeman da rawar da ya taka a kakar da ta gabata kuma sun yanke hukuncin yin gyara akan wasu daga cikin matsalolin da suka fuskanta, yayin da akasarin Daraktocin suka bayyana goyan bayan cigaba da tafiya da manajan.

Shugaban kungiyar ya yaba da dattakon da manajan ya nuna kuma dama sun san shi da irin wadannan halaye na kwarewa, yayin da suke fatar ganin sun samu cigaba a kaka mai zuwa.

Rahotanni sun ce daukar Sergio Aguero daga kungiyar Manchester City na daga cikin dalilan da suka sanya tauraron kungiyar Lionel Messi sauya matsayin sa na cigaba da zama a kungiyar bayan a shekarar da ta gabata ya gabatar da takardar neman sauya sheka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.