Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon Kafa

Kante na takarar lashe kyautar gwarzon dan wasa

‘Yan wasan Chelsea biyu da suka hada da N’Golo Kante da Jorginho na cikin jerin ‘yan wasan da Hukumar Kwallon Kafa ta Turai ta zayyana sunayansu domin zaben gwarzo shekara daga cikinsu da ya cancaci lashe kyautar  hukumar a bana.

N'Golo Kante ya taimaka wa Chelsea lashe kofin zakarun Turai.
N'Golo Kante ya taimaka wa Chelsea lashe kofin zakarun Turai. Matt Dunham POOL/AFP/File
Talla

Kazalika akwai Kevin De Bruyne na Manchester City a cikin masu takarar lashe kyautar gwarzon dan wasan na kakar 2020 zuwa 2021.

Kante da Jorginho sun taka gagarumar rawa a wasan da Chelsea ta doke Manchester City da cin 1-0 a birnin Porto a cikin watan Mayu, abin da ya sa Chelsea din ta lashe kofin zakarun Turai.

A ranar Alhamis mai zuwa ne za a gudanar da bikin ayyana wanda za a mika wa kyautar a birnin Santanbul na Turkiya.

Kazalika a wannan ranar ce kuma, Hukumar ta UEFA za ta fitar da sabon jadawalin gasar cin kofin kasashen Turai ta bana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.