Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon Kafa

Zan dawo da martabar Barcelona - Hernandez

Kocin Barcelona Xavi Hernandez ya lashi takobin dawo da martabar kungiyar a matakin kololuwa a nahiyar Turai, bayan da Bayern Munich ta fitar da su daga gasar cin kofin zakarun Turai, inda ta lallasa su da ci 3-0.

Xavi Hernandez
Xavi Hernandez Fayez Nureldine AFP/Archives
Talla

A karon farko kenan cikin shekaru 21 da ake yin waje da Barcelona a matakin rukuni a gasar ta zakarun Turai.

Tun kakar shekara ta 2003-04, Barcelona ke kaiwa matakin kuniyoyi 16 a gasar, amma a wannan karon al’amarin ya sauya.

Kocin na Barcelona ya ce, yana cikin fushi, kuma ba ya jin dadin abin da ke faruwa da kungiyar a yanzu, yayin da ya kara da cewa, daga yanzu za su bude sabon babi na daga darajar kungiyar wadda ta lashe kofin zakarun Turai sau biyar.

Ko a wasansu zagaye na farko a Camp Nou a cikin watan Satumba, sai da Bayern Munich ta yi wa Barcelona ci 3-0.

Tuni jaridun Sifaniya suka yi ta yi wa Barcelona raddi kan rashin tabuka abun kirki, inda jaridar AS ta bayyana ficewar Barelonar a matsayin murabus din kungiyar daga kwallon kafa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.