Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon Kafa

Zakarun Turai: Benzema na fatan fafatawa a wasan Madrid da PSG

Karim Benzema yana da yakinin cewa zai samu kuzarin da zai fafata a wasan kungiyarsa,  Real Madrid da Paris Saint-Germain a wasan gasar zakarun nahiyar Turai in an jima a Talatar nan, bayan da ya yi jinyar rauni a kafarsa.

Karim Benzema ya ci wa Real Madrid kwallaye 24 a wanna kaka.
Karim Benzema ya ci wa Real Madrid kwallaye 24 a wanna kaka. JAVIER SORIANO AFP
Talla

A jiya Litinin dan wasan gaban na Real Madrid ya shaida wa manema labarai cewa ya ji garau, kuma yana jin cewa za a iya damawa da shi.

Benzema, wanda shine dan wasan da ya fi kowa saka kwallaye a raga a Real Madrid, inda ya ci kwallaye 24 a dukkan gasa, bai buga wa kungiyar tasa wasanni 3 ba tun bayan da ya fita daga fili yana dingishi a wasan da suka barje gumi da Elche 2-2 a ranar 23 ga watan Janairu.

Benzema ya ce fafatawarsa da kylian Mbappe a bangaren PSG wani abu ne na musamman a gareshi, duba da yadda ake ta rade radin zai koma Madrid, da kuma ganin cewa dukkanninsu su na yi wa tawagar Faransa wasa.

Bangarorin 2 za su hadu ne a filin wasa na Parc des Princes, kana su yi fafatawa ta 2 a Madrid ranar 9 ga watan Maris.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.