Neymar zai tafi hutun jinyar watanni hudu - PSG
Hukumomin gudanarwar Paris Saint-Germain ta kasar Faransa, sun fitar da sanarwar cewa dan wasan Brazil Neymar zai tafi hutun jinya, har tsawon watanni uku zuwa hudu.
Wallafawa ranar:
Talla
Sanarwar ta ce za a yi wa dan wasan aiki a kafarsa, bayan rauni da ya samu.
Neymar wanda ya samu raunin a ranar 19 ga watan Fabrairu, yayin wasan su da Lille a gasar Ligue 1, ta kasar Faransa, a ‘yan shekarun nan ya sha fama da ciwo a kafarsa ta dama.
Kulob din na Faransa ya ce likitoci sun bayar da shawarar a yiwa dan wasan aiki a wani asibiti da ke Doha, babban birnin kasar Qatar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu