Isa ga babban shafi

Al Nassr ta sallami kocinta kasa da shekara guda bayan kama aiki

Kungiyar Al Nassr da ke Saudiya ta sallami kocinta dan Faransa Rudi Garcia, a ranar Alhamis

Tsohon mai horas da kungiyar Al Nassr da ke gasar kwallon kafar kasar Saudiya
Tsohon mai horas da kungiyar Al Nassr da ke gasar kwallon kafar kasar Saudiya REUTERS - AHMED YOSRI
Talla

Cikin sanarwar da ta fitar, Al Nassr ta ce ta raba gari da kocin ne bayan fahimtar juna da suka yi akan cewa matakin ne mafi dacewa a yanzu.

A watan Yulin da ya gabata Al Nassr ta kulla yarjejeniya da Garcia, mai shekaru 59, kuma ya bar kungiyar ne yanzu haka ta na kan matsayi na biyu a gasar kwallon kafa ta Saudiya maki uku tsakaninta da abokiyar hamayyarta Al Ittihad.

Garcia ya taba horas da kungiyoyin Lille da Marseille da kuma Lyon a kasarsa Faransa, ya kuma shafe shekaru biyu da rabi yana horar da kungiyar AS Roma a Italiya tsakanin shekarar 2013 zuwa 2016.

A karkashin tsohon kocin ne Al Nassr ta kulla yarjejeniya da Cristiano Ronaldo a watan Disamba kan yarjejeniyar biyansa sama da Yuro miliyan 400 a tsawaon shekaru biyu.

Ya zuwa yanzu Ronaldo ya ci wa kungiyar ta sa kwallaye 11 a wasanni 12 da ya buga.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.