Isa ga babban shafi
AFCON

Karon farko tawagar Burkina Faso ta samu nasara a wasan farko na gasar AFCON

Kwallon da Bertrand Traore ya jefa a ragar Mauritania a bugun daga kai sai mai tsaron gida a minti na 95, ta bai wa tawagar Burkina Faso nasara a wasan farko da tawagar ta yi a rukunin D.

Bertrand Traore, a lokacin da yake murnar jefa kwallon a ragar Mauritania.
Bertrand Traore, a lokacin da yake murnar jefa kwallon a ragar Mauritania. © AFP / KENZO TRIBOUILLARD
Talla

Wannan ne dai karo na farko da tawagar Burkina Faso ta samu nasara a wasan farko cikin yunkuri 13, a gasar lashe kofin Afrika.

Burkina Faso ce ta mamaye wasan, duk da cewa Mauritania ta samu damarmaki amma kuma ta gasa jefa koda kwallo guda.

Dan wasan gaba na tawagar Mauritania Hemeya Tanji a lokacin karawarsu da Burkina Faso.
Dan wasan gaba na tawagar Mauritania Hemeya Tanji a lokacin karawarsu da Burkina Faso. © AFP / KENZO TRIBOUILLARD

Da wannan nasara ta Burkina Faso, a yanzu ita ke jagorantar rukunin D da maki 3, ganin yadda Algeria da Angola su ka tashi 1-1.

A cikin gasar AFCON biyar da aka yi a baya bayan nan, sau uku tawagar Burkina Faso na kai wa wasan kusa dana karshe.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.