Isa ga babban shafi

Al Nassr ta Ronaldo ta fice daga gasar cin kofin zakarun Asiya

Ronaldo da tawagarsa ta Al Nassr sun fice daga gasar zakarun Asia.Duk da cewa Cristiano Ronaldo ya zura kwallo a karin lokaci amma kungiyar Al Nassr ta fice daga gasar cin kofin zakarun nahiyar Asiya sakamakon kashi da ta sha a hannun Al Ain a bugun fanariti ranar Litinin.

Dan wasan gaba na Al Nassr na kasar Saudiya, Christiano Ronaldo.
Dan wasan gaba na Al Nassr na kasar Saudiya, Christiano Ronaldo. REUTERS - AHMED YOSRI
Talla

Dan kasar Portugal mai shekaru 39, shi ne dan wasan Al Nassr daya tilo da ya zura kwallo a bugun daga kai sai mai tsaron gida, yayin da tawagarsa ta Saudiyya ta tashi 3-1 a bugun fenareti, bayan 4 da 4 a wasan gida da waje.

Wannan dare ne mai cike da takaici ga tsohon dan wasan gaban na Manchester United da Real Madrid.

Haduwar farko an doke Al Nasr da 1-0 a Hadaddiyar Daular Larabawa, a wasan na daren Litinin kuwa a mintuna na 118 Ronaldo ya farke kwallo aka tashi wasa Al Nasr na ci 4-3, abin da ya kai aka tafi bugun finareti, kuma ‘yan tawagarsa biyu suka barar sai shi kadai ya ci aka karkare 3 -1.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.