A wani Rahoton Hukumar kula da Ci gaba ta Majalisar Dinkin Duniya, Rahoton ya bayyana cewa duk da ci gaban tattalin arzikin da Afrika ta samu a cikin shekaru goma da suka gabata, Yankin na fama da matsalar yunwa.
Talla
Rahotan yace, babu yadda za’a san Afrikan na samun ci gaba, idan dai ba a bunkasa harkar noma da samar da abinci ba, domin wadata kasashe 27 daga cikin 53 da ke nahiyar, masu fama da yunwa.
A cikin shirin, Bashir Ibrahim Idris tare da abokan shi, sun tattauna game da wannan batu akan yadda za’a shawo kan matsalar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu